Tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya yi kira da a yi gyara ga dokar zabe ta 2022

Tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya yi kira da a yi gyara ga dokar zabe ta 2022.

Ya ce duk da cewa dokar zaben kasar za a iya cewa ita ce mafi inganci a tarihin Najeriya, amma ba ta cika ba; kuma akwai bukatar karin gyara.

Jega ya yi wannan jawabi ne a wani taron kwana biyu da Cibiyar Nazarin Majalisun Dokoki da Dimokuradiyya (NILDS) ta shirya wa Sanatoci a Ikot Ekpene, Jihar Akwa Ibom.
Gyare-gyaren, in ji shi, ya kamata su sanya watsar da sakamako ta hanyar na'urar Mai anfani da lantarki ta daga zabuka masu zuwa a shekarar 2027.
Ya kuma ce kamata ya yi ace ba shugaban kasa ne ke  nada shugaba da kwamishinonin INEC na kasa ba domin kwato hukumar daga bangaranci.
Ya ce kamata ya yi a sake duba dokar domin tabbatar da cewa an warware duk wasu al’amura da suka taso daga gudanar da zabe tare da yanke hukunci kafin ranar da za a rantsar da su.



Comments

Popular posts from this blog

Daga Kamfanin A.S.U Media -- Sakon taya murnan samun Sarautan Wazirin katagum.

Sanata Halliru Dauda Jika ya sauya Sheka daga Jam'iyyar NNPP zuwa Jam'iyyar APC.

Dan Majalisan Tarayya,Ya rabawa Al'ummar Mazabar sa bututun magudanar: Masai.Hon Aminu Aliyu Gari